ha_obs/content/40.md

2.6 KiB

40. An Gicciye Yesu

OBS Image

Bayan sojojin sun yi wa Yesu ba'a, sai suka tafi da shi domin su gicciye shi. Suka sa shi ya dauki gicciyen da zai mutu akai.

OBS Image

Sojojin suka kawo Yesu wurin da ake kira, "Kokon kai" suka kafe hannayensa da kafafunsa da kusa akan gicciye. Amma Yesu ya ce, "Uba ka gafarta masu domin basu san abin da suke yi ba." Bilatus ya bada umarni su rubuta, "Sarkin Yahudawa" akan allo su kuma sa shi akan gicciyen, sama da kan Yesu.

OBS Image

Sojojin suka yi kuri'a akan tufafin Yesu. Sa'anda suka yi haka, sun cika wani annabci da ya ce, "Sun raba tufafina a tsakaninsu, suka sa kuri'a akan tufa ta."

OBS Image

Aka gicciye Yesu tsakanin 'yan fashi biyu. Daya daga cikinsu ya yi wa Yesu ba'a, amma dayan ya ce, "Baka da tsoron Allah? mu mun yi laifi amma wannan mutumin bashi da laifi." Sa'anan ya ce wa Yesu, "In ka yarda ka tuna da ni a mulkinka." Yesu ya amsa masa. "Yau zaka kasance tare da ni a fiddausi."

OBS Image

Shugbannin Yahudawa da wadansu mutane a cikin taron suka yi wa Yesu ba'a. Suka ce masa, "Idan kai 'Dan Allah ne sauko daga kan gicciyen ka ceci kanka! sa'annan zamu gaskanta ka."

OBS Image

Sai sararin sama na lardin ya yi baki gaba daya, ko da yake da tsakiyar rana ne. Wuri ya zama duhu da tsakar rana, aka kuma ci gaba da duhu har sa'a uku.

OBS Image

Sa'anan Yesu yi kuka, "Ya kare! Uba na bada ruhu na a cikin hannun ka." Sai ya sunkuyar da kansa ya saki ruhunsa. Da ya mutu an yi girgizar kasa, sai babban labulen da ya raba mutane da Allah a Haikali, ya tsage biyu, daga sama zuwa kasa.

OBS Image

Ta wurin mutuwarsa, Yesu ya bude hanya da mutane za su zo gun Allah. Da sojan nan mai tsaron Yesu ya ga dukkan abubuwan da suka faru, sai ya ce, "Hakika, wannan mutumin marar laifi ne. Shi Dan Allah ne."

OBS Image

Sa'annan Yusufu da NIkodimas, shugabannin Yahudawa biyu wadanda suka gaskanta, Yesu Almasihu ne, suka tambayi Bilatus jikin Yesu. Suka nade jikinsa cikin zani suka sa shi cikin kabarin dutse da aka sassaka. Sa'anan suka mirgina babban dutse a bakin kabarin domin su rufe kofar.

Labari a Littafi Mai Tsarki daga: Matta 27: 27-61; Markus 15: 16-47; Luka 23:26-56; Yahaya 19: 17-42