ha_obs/content/36.md

32 lines
1.8 KiB
Markdown

# 36. Sakewar Kamanni
![OBS Image](https://cdn.door43.org/obs/jpg/360px/obs-en-36-01.jpg)
Wata rana, Yesu ya dauki uku daga cikin almajiransa, Bitrus, Yakubu, da Yahaya. (Almajirin nan mai suna Yahaya ba shine wanda yayi wa Yesu baftisma ba.) Sun hau kan dutse mai tsawo domin su yi addu'a su kadai.
![OBS Image](https://cdn.door43.org/obs/jpg/360px/obs-en-36-02.jpg)
Da Yesu yana addu'a, sai fuskarsa tayi annuri (Haske) kamar rana kuma tufafinsa suka zama fari fat, fiye da yadda wani a duniya zai maishe su.
![OBS Image](https://cdn.door43.org/obs/jpg/360px/obs-en-36-03.jpg)
Sa'annan Musa da annabi Iliya suka bayyana. Wadannan mutane sun yi zama a duniya daruruwan shekaru kafin lokacin nan. Sun yi magana da Yesu game da mutuwarsa, wanda zai faru ba da dadewa ba a Urushalima.
![OBS Image](https://cdn.door43.org/obs/jpg/360px/obs-en-36-04.jpg)
Yayin da Musa da Iliya ke magana da Yesu, Bitrus yace wa Yesu, "Yana da kyau da muke a nan. Bari mu kafa bukkoki uku, daya na ka, daya na Musa, daya kuma na Iliya." Bitrus bai san abinda yake fada ba.
![OBS Image](https://cdn.door43.org/obs/jpg/360px/obs-en-36-05.jpg)
Yayin da Bitrus ke magana, girgije mai haske ta sauko ya lullube su sai murya daga girgijen ya ce, "Wannan shine dana wanda nake kauna. Ina farin ciki da shi. Ku saurare shi." Almajiran nan uku suka razana suka fadi kasa.
![OBS Image](https://cdn.door43.org/obs/jpg/360px/obs-en-36-06.jpg)
Sai Yesu ya taba su ya ce, "Kada ku ji tsoro. Ku tashi." Sa'anda suka duba kewaye, sai Yesu shi kadai ke wurin.
![OBS Image](https://cdn.door43.org/obs/jpg/360px/obs-en-36-07.jpg)
Yesu tare da almajiran nan uku suka sauka daga dutsen. Sai Yesu yace masu, "Kada ku gaya wa kowa abinda ya faru anan tukunna. Bada dadewa ba, zan mutu in kuma sake rayuwa. Bayan haka, zaku iya fada wa mutane."
_Labari a Littafi Mai Tsarki daga: Matta 17:1-9; Markus 9:2-8; Luka 9:28-36_