ha_obs/content/34.md

2.7 KiB

34. Yesu ya Koyar da Wassu Labaru

OBS Image

Yesu ya fadi wadansu labaru da yawa game da Mulkin Allah. Misali, yace, "Mulkin Allah kamar kwayar mastad ya ke da wani ya shuka a gonarsa. Kun sani cewa kwayar mastad ita ce mafi kankanta dukka cikin iri."

OBS Image

"Amma sa'anda kwayar mastad ya girma, sai yafi dukkan itatuwan dake gona girma, kuma da girma sosai harma tsuntsaye sukan zo su huta a cikin rassan sa."

OBS Image

Yesu ya sake fadin wani labari, "Za'a kwatanta mulkin Allah da yistin da mace ke kwabawa cikin curin gurasa har sai ya mamaye dukka curin."

OBS Image

Haka kuma mulkin Allah kamar dukiya ce da wani ya boye a wani fage. Wani mutum dabam ya sami dukiyar shi ma ya sake binne ta. Yana cike da murna harma ya je ya sayar da dukkan mallakar sa, ya yi amfani da kudin don ya sayi filin."

OBS Image

"Haka kuma mulkin Allah kamar lu'u lu'u ne mai darajar gaske. Sa'anda dillalin lu'u lu'u ya same ta, sai ya sayar da dukkan mallakar sa ya yi amfani da kudin domin ya saye ta.''

OBS Image

Sa'annan Yesu ya fadi wani labari wa mutane da suke dogara da ayyukan su nagari amma su na raina sauran mutane. Yace, "Mutane biyu suka je haikali don su yi addu'a. Daya mai karbar haraj i ne, dayan kuma shugaban addini ne."

OBS Image

"Shugaban addinin yayi addu'a kamar haka, 'Na gode maka Allah, domin ni ba mai zunubi bane kamar sauran mutane, barayi, marasa adalci, mazinata, ko kuma kamar wancen mai karban haraji.'''

OBS Image

'''Misali, na kan yi azumi sau biyu ko wace mako, nakan kuma baka daya bisa goma cikin dukkan kudi da kayayyakin da na karba."'

OBS Image

"Amma mai karbar harajin ya tsaya nesa da shugaban addini, baya ma duban sama. A maimakon haka, ya dunkula hannu yana buga girjinsa ya yi addu'a, 'Allah, yi mani jinkai domin ni mai zunubi ne.'''

OBS Image

Sai Yesu yace, "Gaskiya nake gaya maku, Allah ya ji addu'ar mai karban harajin nan ya kuma ce da shi adali. Amma bai so addu'ar shugaban addinin nan ba. Allah zai kaskantar da duk mai fahariya, ya kuma daukaka duk wanda ya kaskantar da kansa."

Labari a Littafi Mai Tsarki daga: Matta 13:31-33, 44-46; Markus 4:30-32; Luka 13:18-21; 18:9-14