ha_obs/content/30.md

2.4 KiB

30. Yesu ya Ciyar da Mutane Dubu Biyar.

OBS Image

Yesu ya aiki manzaninsa su yi wa'azi da koyarwa a kauyuka dabam-dabam masu yawa. Da suka dawo, wurin da Yesu yake, suka gaya masa abin da suka yi. Sai Yasu ya gayyace su, su je wani wuri tare da shi a kebe a ketaren tafki domin su huta a can na dan lokaci. Sai, suka shiga jirgin ruwa suka ketare zuwa gaccin tafkin.

OBS Image

Amma akwai mutane da yawa da suka ga Yesu da almajiran sa sun tafi a jirgin ruwan. Wadannan mutanen suka ruga suka bi bakin tafkin domin su riga su zuwa dayan tsallaken. Yayin da Yesu da almajiran sa suka isa can, taron mutane da yawa na nan suna jiran su.

OBS Image

Taron na da maza fiye da 5,000, ba a ma kirga mata da yara ba. Yesu ya yi juyayi kwarai game da mutanen. Ga Yesu, mutanen nan na kama suke da tumaki da basu da makiyayi. Saboda haka ya koyar da su, ya kuma warkar da wadan da suke da rashin lafiya a cikin su.

OBS Image

Can da yamma, almajiran suka ce wa Yesu, "Lokaci ya kure kuma ba garuruwa kusa. Ka sallami mutanen domin su je su sami abinda za su ci."

OBS Image

Amma Yesu ya ce wa almajiran, "Ku ba su abinda za su ci!" Suka ansa da ce wa, "Ya ya zamu yi haka? Muna da curin gurasa biyar da 'yan kifi biyu."

OBS Image

Yesu ya ce wa almajiran sa, su ce wa mutanen dake taron su zauna a kan ciyawa, a rukunin mutane hamsin hamsin.

OBS Image

Sa'annan Yesu ya dauki gurasa biyar da kifi biyun, ya duba sama, ya kuma godewa Allah domin abincin.

OBS Image

Sai, Yesu ya gutsuttsura gurasar da kifin. Ya ba wa almajiran sa, don su ba wa mutanen. Almajiran su ka ci gaba da mika abincin, bai kuma kare ba! Dukkan mutanen suka ci suka kuma koshi.

OBS Image

Bayan haka, almajiran suka tattara sauran abincin da ba'a ci ba, ya kuma isa ya cika kwanduna goma sha biyu! Dukkan abincin nan ya samu ne daga gurasa biyar da kifi biyun.

Labari a Littafi Mai Tsarki daga: Matta 14:13-21; Markus 6:31-44; Luka 9:10-17; Yahaya 6:5-15