ha_obs/content/28.md

2.6 KiB

28. Saurayi Shugaba Mai arziki

OBS Image

Wata rana, wani saurayi mai arziki shugaba ya zo wurin Yesu, ya yi masa tambaya, "Malam Managarci me zan yi domin in sami rai madawwami?'' Yesu ya ce masa, ''Don me ka kira ni 'managarci'? Managarci daya ne, shine Allah. Amma Idan kana so ka sami rai madawwami, kayi biyayya da dokokin Allah.''

OBS Image

Yayi tambaya, ''Wadanne ne nake bukata in yi biyayya da su?'' Yesu ya amsa, ''Kada ka yi kissan kai. Kada ka yi zina. Kada ka yi sata. Kada ka yi karya. Ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka, sannan ka kaunaci makwabcin ka kamar yadda ka ke kaunar kanka.''

OBS Image

Amma saurayin ya ce, ''Na yi biyayya da dukkan wadannan dokokin tun ina dan yaro. Me nake bukata kuma in yi domin in rayu har'abada?'' Yesu ya kalle shi ya kaunace shi.

OBS Image

Yesu ya amsa, ''Idan kana so ka zama cikakke, to, ka je ka sayar da dukkan mallakar ka, ka ba wa talakawa kudin, za ka sami dukiya a sama. Sa'annan ka zo ka bi ni.''

OBS Image

Da saurayin ya ji abin da Yesu ya fada, sai ya cika da bakin ciki, domin shi mai arziki ne sosai, kuma bai so ya ba da dukkan mallakarsa ba. Sai ya juya ya tafi daga wurin Yesu.

OBS Image

Sai Yesu ya ce wa almajiransa, "Yana da wuya kwarai ga mutane masu arziki su shiga mulkin Allah! I, ya fiye sauki rakumi ya shiga ta ramin allura, da mai arziki ya shiga mulkin Allah.''

OBS Image

Sa'anda almajiran suka ji abin da Yesu ya fada, sai suka yi mamaki suka ce, "To wanene zai sami ceto?''

OBS Image

Yesu ya dubi almajiran , ya ce, ''Ga mutane wannan ba shi yiwuwa, amma da Allah kome mai yiwuwa ne.''

OBS Image

Bitrus ya ce wa Yesu, ''Mun bar kome mun bi ka, me zai zama sakamakon mu?''

OBS Image

Yesu ya amsa, ''Duk wanda ya bar gidaje, 'yan'uwa maza, da mata, uba da uwa, da 'ya'ya ko mallaka saboda ni, zai sami sama da ribi 100, ya kuma sami rai madawwami. Amma dayawa dake na farko za su zama na karshe, kuma wadanda ke na karshe za su zama na farko.''

Labari a Lttafi Mai Tsarki daga: Matta 19:16-30; Markus 10:17-31; Luka 18:18-30