ha_obs/content/25.md

36 lines
1.9 KiB
Markdown

# 25. Shaidan ya jarabci Yesu
![OBS Image](https://cdn.door43.org/obs/jpg/360px/obs-en-25-01.jpg)
Nan da nan bayan an yi wa Yesu baftisma, Ruhu Mai Tsarki ya bishe Yesu zuwa jeji, in da ya yi azumi kwanaki da dare arba'in, sai Shaidan ya zo wurin Yesu ya jarabce shi domin ya yi zunubi.
![OBS Image](https://cdn.door43.org/obs/jpg/360px/obs-en-25-02.jpg)
Shaidan ya jarabci Yesu yana cewa, in kai ne dan Allah, ka mai da duwatsun nan gurasa, don ka ci
![OBS Image](https://cdn.door43.org/obs/jpg/360px/obs-en-25-03.jpg)
Yesu amsa ya ce, "A rubuce ya ke a kalmar Allah, 'Mutane basu bukatar gurasa kawai don su rayu, amma suna bukatar kowace kalma da Allah yake fada!"'
![OBS Image](https://cdn.door43.org/obs/jpg/360px/obs-en-25-04.jpg)
Sa'annan Shaidan ya dauki Yesu ya kai shi saman haikali a wurin da ya fi tsawo duka, ya ce masa, "In kai ne dan Allah ka yi tsalle daga nan zuwa kasa, domin a rubuce yake, 'Allah zai umurci mala'ikunsa su tallafe ka domin kada kafanka ya yi tuntube da dutse.'''
![OBS Image](https://cdn.door43.org/obs/jpg/360px/obs-en-25-05.jpg)
Amma Yesu ya amsa wa Shaidan da abinda aka rubuta daga cikin Nassi. Ya ce, "A kalmar Allah, ya umurci mutanensa, 'Kada ku gwada Ubangiji Allahn ku."'
![OBS Image](https://cdn.door43.org/obs/jpg/360px/obs-en-25-06.jpg)
Sai Shaidan ya nuna wa Yesu dukkan mulkokin duniya da dukkan daukakarsu kuma ya ce, "Zan baka dukkan wannan, idan ka rusuna ka yi mani sujada."
![OBS Image](https://cdn.door43.org/obs/jpg/360px/obs-en-25-07.jpg)
Yesu amsa "Rabu da ni, shaidan! A kalmar Allah ya umurci mutanensa, 'Ku yi wa Ubangiji Allahn ku sujada shi kadai kuma za ku bauta wa"'
![OBS Image](https://cdn.door43.org/obs/jpg/360px/obs-en-25-08.jpg)
Yesu bai fada cikin jerabobin Shaidan ba, saboda haka Shaidan ya rabu da shi. Sai mala'iku suka zo suka yi wa Yesu hidima.
_Labari a Littafi Mai Tsarki Daga: Matiyu 4:1-11; Markus 1:12-13; Luka 4:1-13_