ha_obs/content/23.md

3.1 KiB

23. Haihuwar Yesu

OBS Image

Maryamu tana da alkawarin aure da wani adali mai suna Yusufu. Sa'anda ya ji cewa Maryamu tana da juna biyu, ya sani cewa jaririn dake cikin ta ba na sa bane. Baya so ya kunyatar da Maryamu, sai ya yi shirin ya saketa a asirce. Kafin ya yi haka, Mala'ika ya zo ya yi magana da shi a mafarki.

OBS Image

Mala'ikan yace, "Yusufu, kada ka ji tsoron daukar Maryamu, a matsayin matar ka. Jaririn dake cikinta daga Ruhu Mai Tsarki ne. Zata haifi 'da. Ka sa masa suna Yesu (ma'ana, 'Yahweh mai ceto'), domin zaya ceci mutane daga zunuban su."

OBS Image

Sai Yusufu ya auri Maryamu ya kuma kawo ta gida a matsayin matarsa, amma bai santa ba, har sai da ta haihu.

OBS Image

Sa'adda Maryamu ta kusa haihuwa, sai masu mulkin Roma suka umurci kowa ya je kidaya a birnin da kakanninsu suka zauna. Yusufu da Maryamu suka yi tafiya mai nisa daga inda suke zama a Nazaret, zuwa Baitalami domin Dauda ne kakan su, kuma Baitalami ne garin su.

OBS Image

Da suka isa Baitalami, ba su sami masauki ba. Dakin da suka samu kawai shine mazaunin dabbobi. Aka haifi jaririn a wurin, mahaifiyar kuma ta shimfida shi a kwami, da shike basu da gado domin shi. Suka sa masa suna Yesu.

OBS Image

Cikin daren nan, akwai wadansu makiyaya a fage kusa da su suna tsaron dabbobin su. Nan da nan, wani mala'ika mai walkiya ya bayyana a gare su, sai suka firgita. Sai mala'ikan ya ce, "Kada ku ji tsoro, domin ina da labari mai dadi domin ku. An haife Almasihu, Ubangiji, a Baitalami!"

OBS Image

''Ku je ku nemi jaririn, za ku kuma same shi a nannade cikin tsummokara yana kwance a kwami." Nan da nan, sararin sama ta cika da mala'iku suna girmama Allah, suna cewa, "Daukaka ta tabbbata ga Allah a sama, da salama a duniya, ga mutanen da ya yi wa tagomashi!"

OBS Image

Nan da nan makiyayan kuwa suka iso wurin da Yesu yake, sai suka same shi a kwance cikin kwami, kamar yadda mala'ikan ya fada masu. Su ka cika da murna. Makiyayan suka koma fagen da tumakansu suke, su na yabon Allah domin dukkan abubuwan da suka ji suka kuma gani.

OBS Image

Bayan wani lokaci, masana daga kasashe masu nisa a gabas, suka ga wani bakon tauraro a sararin sama. Suka gane cewa ma'anar haka itace an haifi sabon sarkin Yahudawa. Sai suka yi tafiya mai nisa domin su ga wannan sarkin. Suka zo Baitalami suka sami gidan da Yesu da iyayensa suke zama.

OBS Image

Sa'anda masanan suka ga Yesu da mahaifiyar sa, sai suka rusuna suka yi masa sujada. Suka ba wa Yesu kyautai masu tsada. Sa'annan suka koma gida.

Labari a Litafi Mai Tsarki daga: Matta 1; Luka 2