ha_obs/content/17.md

60 lines
5.2 KiB
Markdown

# 17. Alkawarin Allah da Dauda
![OBS Image](https://cdn.door43.org/obs/jpg/360px/obs-en-17-01.jpg)
Saul shi ne sarki na farko a Isar'ila. mai tsayi ne shi, kyakkyawa ne kamar yarda mutane ke so. Saul sarki ne na gari a farkon shekaru a mulkinsa bisa Isar'ila. Amma ya zama mugu mutum wanda ba ya biyayya da Allah, Allah ya zabi wani mutum dabam wanda wata rana zai zama sarki amadadinsa.
![OBS Image](https://cdn.door43.org/obs/jpg/360px/obs-en-17-02.jpg)
Allah ya zabi wani matashin Isar'ila, mai suna Dauda ya zama sarki bayan Saul. Dauda makiyayi ne daga garin Baitalami . A lokaci dabam dabam yayin da yake kiwon tumakin mahaifinsa, Dauda ya kashe zaki da biyer da su ka kai hari ga tumakin. Dauda mutum ne mai tawali'u da adalci wanda ya dogara yana kuma biyayya da Allah.
![OBS Image](https://cdn.door43.org/obs/jpg/360px/obs-en-17-03.jpg)
Dauda ya zama jarumin soja da kuma shugaba. Sa'anda Dauda ke matashi, ya yi fada da katon nan mai suna Goliya. Goliya hurarren soja ne, kakkarfa tsayinsa misali kamu uku! Amma Allah ya taimake Dauda ya kashe Goliya, ya kuma ceci Isar'ila. Bayan wancen, Dauda ya yi nasarori da yawa akan abokan gaban Isar'ila, don wannan mutane ke yabon sa.
![OBS Image](https://cdn.door43.org/obs/jpg/360px/obs-en-17-04.jpg)
Saul yana kishi da kaunar da mutane ke yi wa Dauda. sau da yawa Saul ya yi kokarin kashe shi, sai Dauda ya boye wa Saul . Wata rana, Saul na neman Dauda domin ya kashe shi. Saul ya je kogon da Dauda ke boye wa daga Saul, Amma Saul bai gan shi ba. Amma Dauda na nan kusa da inda Saul ya ke, zai iya kashe shi, amma bai yi ba. Maimakon haka, Dauda ya dauke yankin rigar Saul ya tabbatar ma sa cewa ba zai kashe shi don ya zama sarki ba.
![OBS Image](https://cdn.door43.org/obs/jpg/360px/obs-en-17-05.jpg)
Bayan mutuwar Saul a yaki, sai Dauda ya zama sarkin Isar'ila. Shi sarki ne na gari, kuma mutane na kaunarsa. Allah ya albarkace Dauda, ya kuma bunkasa. Dauda ya yi yake yake da dama, Allah ya kuma taimake shi ya ci nasara akan abokan gaba na Isar'ila. Dauda ya ci nasara abisa Urushalima ya mishe shi babban barin kasarsa. Alokacin da Dauda ke mulkin, Isar'ila sun zama masu iko da arziki.
![OBS Image](https://cdn.door43.org/obs/jpg/360px/obs-en-17-06.jpg)
Dauda ya so ya gina haikali inda dukan Isar'ilawa za su bauta wa Allah, su kuma mika masa hadayu. Kimanin shekaru dari hudu (400), mutane sukan bautawa Allah, da kuma mika masa hadayu a alfarwa ta saduwa wanda Musa ya gina.
![OBS Image](https://cdn.door43.org/obs/jpg/360px/obs-en-17-07.jpg)
Amma Allah ya aika anabi Nathan zuwa ga Dauda da wannan sako, "Saboda kai dan yaki ne, ba za ka iya gina mani wannan haikalin ba. Danka ne zai gina shi. Amma, zan albarkace ka kwarai. Daya daga zuri'ar zai yi mulki amatsayin sarki bisa mutane na har abada!" Almasihu ne kadai ke da ikon mulki na har abada a zuri'ar Dauda. Almasihu zabbabe dan Allah wanda zai ceci mutanen duniya daga zunubinsu.
![OBS Image](https://cdn.door43.org/obs/jpg/360px/obs-en-17-08.jpg)
Sa'anda Dauda ya ji wadannan kalmomi, Nan da nan ya yi godiya, da yabo ga Allah domin ya yi wa Dauda wannan alkawari mai girma da daraja da albarku masu yawa. Dauda bai san lokacin da Allah zai yi wadannan abubuwa ba. Amma yadda ya kasance, sai Isar'ilawa za su yi jira na tsawon lokaci kafin zuwan Almasihu, kusan shekaru dubu daya (1,000).
![OBS Image](https://cdn.door43.org/obs/jpg/360px/obs-en-17-09.jpg)
Dauda ya yi mulkinsa da adalci da kuma aminci na shekaru da dama, kuma Allah ya albarkace shi. Duk da haka, a karshen rayuwarsa ya yi mummunar zunubi ga Allah.
![OBS Image](https://cdn.door43.org/obs/jpg/360px/obs-en-17-10.jpg)
Wata rana, sa'anda dukan sojojin Dauda sun tafi yaki nisa da gida, ya duba daga cikin fadarsa, sai ya ga wata kyakkyawar mace tana wanka. Mai suna Batsheba.
![OBS Image](https://cdn.door43.org/obs/jpg/360px/obs-en-17-11.jpg)
A maimakon kau da hankalin sa, Dauda ya aika da wani ya kawo ta a gare shi, ya kwana da ta, sai ya sallame ta kuma ta koma agida. Bayan lokaci kadan Batsheba ta aika da sako zuwa ga Dauda cewa tana da juna biyu.
![OBS Image](https://cdn.door43.org/obs/jpg/360px/obs-en-17-12.jpg)
Mai gidan Batsheda, mutum ne mai suna Uriya, yana cikin daya daga kwararon sojojin Dauda. Dauda ya kira Uriya ya dawo daga yaki, sai ya gaya masa ya je ya kasance da matarsa. Amma Uriya ya ki ya je gida, yayin da sauran sojoji na yaki. Sai Dauda ya tura Uriya gurin yaki ya gaya wa shugaban sojojin ya sa shi inda abokan gaba ke da karfi don a kashe shi.
![OBS Image](https://cdn.door43.org/obs/jpg/360px/obs-en-17-13.jpg)
Bayan an kashe Uriya, Dauda ya auri Batsheba.Ta haifa wa Dauda da. Allah ya yi fushi da Dauda a game da abin da ya yi, sai ya aiki Annabi Nathan ya gaya wa Dauda irin mugun zunubi da ya yi. Dauda ya tuba daga zunubinsa kuma Allah ya gafarce shi. Dukkan rayuwar sa, Dauda ya yi tafiya, kuma ya yi biyayya ga Allah, har ma a lokacin tsanani.
![OBS Image](https://cdn.door43.org/obs/jpg/360px/obs-en-17-14.jpg)
Amma, a game da hukuncin zunubin Dauda, dan da ya haifa, ya mutu. Fada tsakanin iyalin Dauda har karshen rayuwar sa, ikon Dauda ya zama mara karfi. Ko da shike Dauda mara aminci ne ga Allah, Allah mai amince ne ga alkawaransa. Daga baya, Dauda da Batsheba son sami wani yaro, su ka sa masa suna Sulaimanu.
_Labari a Littafi Mai Tsarki daga: 1Samaila 10; 15-19; 24; 31; 2 Samaila 5; 7; 11-12_