ha_obs/content/12.md

3.7 KiB

12. Fitowa

OBS Image

Isra'ilawa sun yi farin cikin barin Masar, sun fita daga bauta, sun kama hanya zuwa kasar alkawari! Masarawa sun ba su duk abin da suka tambaye su, har zinari, azurfa da kaya masu muhimminci, wadansu daga alummai sun gaskata da Allah, suka bi Isra'ilawa sa'anda suka fita daga Masar.

OBS Image

Allah ya bishe su da al'amudin girgije da ke gaban su da rana, wanda ya ke zama al'amudin wuta da dare. Allah yana tare da su kuma yana shiryar da su kowane lokaci sa'anda suke tafiya. Duk abinda za su yi shine su bi shi.

OBS Image

Bayan dan lokaci, Fir'auna da mutanensa suka chanza ra'ayi, sun nemi Isra'ilawa su dawo bauta kuma. Allah ya sa Fir'auna ya taurara zuciyarsa domin dukkan mutane su san cewa shi, Yahweh, shine Allah na gaske, Ikon sa kuma ya sha karfin Fir'auna da allolinsa.

OBS Image

Saboda haka Fir'auna da mayakansa suka bi Isra'ilawa su maishe su bayin su kuma. Da Isra'ilawa sun gan mayakan Masarawa na zuwa, sai suka gane cewa sun fada tarko tsakanin mayakan Msarawa da jan teku. Sai suka tsorata sosai, suka yi kuka, "Me ya sa muka bar Masar? Zamu mutu!"

OBS Image

Musa ya ce wa Isra'ilawa, "Ku bar jin tsoro! Allah zai yi yaki domin ku yau kuma zai cece ku." Sai Allah ya ce wa Musa, "Ka gaya wa Isra'ilawa su yi gaba su nufi jan tekun."

OBS Image

Sai Allah ya matsar da al'amudin girgije ya saka shi tsakanin Isra'ilawa da Masarawa, Masarawa suka kasa ganin Isara'ilawa.

OBS Image

Allah ya ce wa musa ka daga hannunka bisa tekun ka raba ruwayen, sai Allah ya sa iska ta raba tekun zuwa hagu da dama, sai hanya ta kasance a tsakiyan tekun.

OBS Image

Isra'ilawa suka wuce a busassar kasa a tsakiyan tekun da bagon ruwa a kowace gefe.

OBS Image

Allah ya daga al'amudin girgije sama domin Masarawa suka gan Isra'ilawa na tserewa. Sai Masarawa suka yanke shawara su bi su.

OBS Image

Sai suka bi Isra'ilawa akan hanyan da ya ratsa tekun, amma Allah ya sa Masarawa suka tsorata ya kuma sa karusansu sun makalewa. Sai suka yi ihu, "Mu gudu! Allah na yi wa Isra'ilawa yaki!"

OBS Image

Bayan dukkan Isra'ilawa sun ketare zuwa dayan gefen tuken lafiya, Allah ya ce wa Musa sake mika hannun ka. Da ya yi biyayya, sai ruwan tekun ya rufe mayakan Masarawa, ya koma wurinsa kamar da. Dukkan mayakan Masarawa suka nutse.

OBS Image

Sa'anda Isra'ilawa sun gan cewa Masarawa sun mutu, sai suka dogara ga Allah kuma suka gaskanta cewa Musa annabin Allah ne.

OBS Image

Isra'ilawa sun yi murna da farin ciki sosai domin Allah ya cece su daga mutuwa da bauta! Yanzu sun sami yanci su bauta wa Allah. Isra'ilawa suka yi wakoki masu yawa, suna bukin samun sabuwar yancin su, sun yi yabon Allah domin ya cece su daga mayakan Masarawa.

OBS Image

Allah ya umurci Isra'ilawa su yi bukin idin ketarewa a kowace shekara domin tunawa da nasara da ya basu bisa Masarawa da kuma ceton su daga bauta. Sun yi bukin tawurin yanka dan rago marar lahani, da cin gurasa mara yeast.

Labari a Littafi Mai Tsarki daga: Fitowa 12:33-15:21