ha_obs/content/09.md

3.8 KiB

9. Allah ya kira Musa

OBS Image

Bayan mutuwar Yusufu, dukkan danginsa sun zauna a Masar. Su da zuri'arsu sun ci gaba da zama awurin shekaru da yawa, kuma suna da 'ya'ya masu yawa, ana kiran su Isra'ilawa.

OBS Image

Bayan shekaru aru-aru, yawan 'ya'yan Isra'ila ya karu sosai. Masarawa sun manta da Yusufu da dukkan aikin da yayi don taimakonsu. Sun ji tsoron Isra'ilawa domin yawansu. Sai Fir'auna da yake mulkin Masar a wannan lokaci ya maishe su bayi ga Massarawa.

OBS Image

Masarawa sun tilasta wa Isra'ilawa suyi gini-gine da yawa har su gina birane gabaki daya. Aiki mai wahalan sa rayuwarsu cikin takaici, amma Allah ya albakaci su, har sun sami karin 'yaya.

OBS Image

Fir'auna ya gani cewa Isra'ilawa suna samun jarirai da yawa, sai ya umurci mutanensa su kashe 'ya'ya maza jarirai ta wurin jefa su cikin Kogin Nilu.

OBS Image

Sai wata bayahudiya ta haifi da namiji. Ita da mijin sun suka boye jaririn iya kokarin su.

OBS Image

Da ya zama iyayen yaron baza su iya boye shi kuma ba, sai suka sa shi cikin Kwandon da baya nustewa tsakanin dogayen ciyayi da suke bakin Kogin Nilu domin su kare shi daga kisa. Baban yar'uwarsa tana kallo ta ga abinda zai faru da shi.

OBS Image

Wata 'yar Fir'auna ta ga Kwandon, ta dubi cikin. Da ta ga jaririn, ta dauke shi a masayin danta. Ta dauki wata bayahudiya yar aiki tayi renon sa ba tare sanin cewa matar mahaifiyar yaron bane. Sa'anda yaron ya kai yayewa, ta mayar da shi wurin 'yar Fir'auna, ta sa masa suna Musa.

OBS Image

Wata rana da Musa ya yi girma, sai ya ga wani bamasare yana dukan Ba-Isra'ile da ke bawa. Musa ya yi kokarin ceton dan'uwansa Ba-Isra'ile.

OBS Image

Musa ya yi tsammanin babu wanda zai gani, sai ya kashe Ba-Masaren ya kuma binne gawar. Amma wani ya ga abinda Musa ya yi.

OBS Image

Da Fir'auna ya ji abin da Musa ya yi, sai ya nemi ya kashe shi. Musa ya gudu daga Masar zuwa jeji inda zai tsere wa sojojin Fir'auna.

OBS Image

Musa ya zama makiyayi a jejin nesa daga Massar. Ya yi aure a nan matar ta haifa masa 'ya'ya maza biyu.

OBS Image

Wata rana, yayin da Musa na kula da tumakin sa, ya ga daji na ci da wuta. Amma dajin bata kone ba. Musa ya je gap da dajin domin ya gani da kyau. Da ya matso kusa da dajin da ke ci da wuta, muryar Allah ya ce, "Musa ka cire takalmanka. Kana tsaye a wuri Mai Tsarki."

OBS Image

Allah ya ce, "Na ga wahalar mutane na. Zan aike ka gun Fir'auna domin ka fitar da Isra'ilawa daga bautar su a Masar. Zan basu kasar Kan'ana. Kasar da na alkawarta wa, Ibrahim, Ishiyaka da Yakubu."

OBS Image

Musa ya yi tambaya, "Idan mutanen sun nemi sanin wanda ya aikoni, me zan ce?" Allah ya ce, "INA NAN YADDA NAKE. Ka gaya masu, 'NI NE ya aiko ni gare ku.' Ka kuma gaya masu, 'ni ne Yahweh, Allah na kakaninku, Ibrahim, Ishaku da Yakubu.' Wannan ne suna har abada."

OBS Image

Musa ya ji tsoro kuma baya so je wurin Fir'auna, domin ya yi tunani cewa, baya iya magana da kyau. sai Allah ya aiki dan'uwan Musa, Haruna, ya taimakeshi. Allah ya gargadi Musa da Haruna cewa Fir'auna ba zai saurare su ba.

Labari a Littafi Mai Tsarki daga: Fitowa 1-4