ha_obs/content/07.md

2.7 KiB

Allah ya albarkaci Yakubu

OBS Image

Sa'anda yayan ke girma, Yakubu yana son zaman gida, amma, Isuwa yana son farauta, Rafkatu tana kaunar Yakubu amma Ishaku yana kaunar Isuwa.

OBS Image

Wata rana, da Isuwa ya dawo daga farauta, yana ji yunwa sosai. Sai ya ce wa Yakubu, "Ba ni daga cikin abincin da ka dafa." Sai Yakubu ya ce masa, "Da farko, ka ba ni matsayinka na dan fari." Sai Isuwa ya ba shi matsayinsa na dan fari. Sa'annan Yakubu ya ba shi abinci.

OBS Image

Ishaku ya so ya ba wa Isuwa albarkarsa. Amma kafin ya yi haka, Rifkatu da Yakubu suka yaudare shi ta wurin sa Yakubu ya badda kamaninsa, kamar shine Isuwa. Ishaku ya tsufa kuma baya ganin. saboda haka, Yakubu ya saka tufafin Isuwa, ya kuma daura fatar akuya a wuyarsa da hannayensa.

OBS Image

Yakubu ya zo wurin Ishaku, ya ce, "Ni ne Isuwa. Na zo domin ka albarkace ni." Da Ishaku ya taba gashin akuyar, ya sunsuna tufafin, sai ya yi tsammanin Isuwa ne, ya kuma albarkace shi.

OBS Image

Isuwa ya ki jinin Yakubu domin ya sace masa damar sa na dan fari, da kuma albarka. Sai ya yi niyyar ya kashe Yakubu bayan mutuwar mahaifinsu

OBS Image

Amma Rifkatu ta ji shirin Isuwa. Sai ita da Ishaku suka tura Yakubu wuri mai nisa, ya zauna da dangin ta.

OBS Image

Yakubu ya zauna da dangin Rifkatu shekaru masu yawa. A wannan lokacin, ya yi aure, ya haifi yaya maza goma sha biyu da ya mace guda daya, Allah ya azurta shi sosai.

OBS Image

Bayan shekaru ashirin da barin gidansa na kan'ana, Yakubu ya komo wurin da iyalinsa, da barorinsa, da dukkan garkin dabbobinsa.

OBS Image

Yakubu ya tsorata sosai domin yana tsamanin har yan zu Isuwa yana so ya kashe shi. Sai ya tura garkunan dabbobi masu yawa kyauta ga Isuwa. Barorin da suka kawo dabbobin suka ce wa Isuwa, "Bawan ka, Yakubu ne, ke baka wadannan dabbobin.Yana zuwa bada jimawa ba.

OBS Image

Amma Isuwa ya rigaya ya yafe wa Yakubu, sun yi murnar sake ganin juna. Sa'annan Yakubu yayi zaman salama a Kan'ana. Sai Ishaku ya rasu, Yakubu da Isuwa suka binne shi. Wa'din alkawaran da Allah ya yi wa Ibrahim ya ci gaba daga kan Ishaku zuwa kan Yakubu.

Labari a Littafi Mai Tsarki daga: Farawa 25:27-33:20