ha_obs/content/05.md

3.1 KiB

5. Dan Alkawari

OBS Image

Bayan shekaru goma da isowar Abram da Saraya cikin Kan'ana, har yanzu basu sami 'da ba. Sai matar Abram, Saraya, ta ce masa, "Tunda Allah bai yarda mini in sami yara ba gashi yanzu na tsufa na kure don haihuwan 'ya'ya, ga baranya ta Hajaratu. Ka aureta domin ta haifi mani da.''

OBS Image

Sai Abram ya auri Hajaratu. Hajaratu ta haifi da namiji, Abram kuma ya bashi suna Isma'ilu. Amma Saratu yi kishin Hajaratu. Da Isma'ilu ya kai shekara 13, Allah ya sake magana da Abram.

OBS Image

Allah ya ce, " Ni ne Allah Mai Iko dukka. Zan yi alkawari da kai." Sai Abram ya yi ruku'u har kasa. Allah kuma ya ce wa Abram, "Zaka zama uban kabilu da yawa. Zan baka da zuriyarka kasar Kan'ana abin gado, kuma zan zama Allahnsu har abada. Dole ka yi wa kowane da namiji a iyalinka kaciya.''

OBS Image

Matarka, Saraya, zata sami da-zai zama dan alkawari. Ka bashi suna Ishaku. Zan yi alkawarina da shi, zai kuma zama babbar kabila. Zan maida Isma'ilu babban kabila kuma, amma alkawarina da Ishaku ne. Sai Allah ya sauya sunan Abram zuwa Ibrahim, ma'ana, "Uban masu yawa." Allah kuma ya sauya sunan Saraya zuwa Saratu, ma'ana, "gimbiya."

OBS Image

A wannan ranar Ibrahim ya yi wa duk mazajen da ke gidansa kaciya. Bayan shekara guda, sa'adda Ibrahim ya kai shekaru 100, Saratu kuma ta yi 90, Saratu ta haifa wa Ibrahim da. Suka bashi suna Ishaku kamar yadda Allah ya gaya masu su yi.

OBS Image

Sa'anda Ishaku ya ke dan saurayi, Allah ya gwada bangaskiyar Ibrahim da cewa, "Dauki Ishaku tilon danka ka kashe shi, ya zama hadaya a gareni." Sai kuma Ibrahim ya yi biyayya da Allah, ya shirya ya yi hadaya da 'dansa.

OBS Image

Sa'anda Ibrahim da Ishaku suke tafiya wurin hadaya, Ishaku ya yi tambaya, "Baba, muna da itace domin hadaya, amma ina dan ragon?'' Ibrahim ya amsa, "Allah zai tanada ragon hadaya, 'dana."

OBS Image

Da suka isa wurin hadaya, Ibrahim ya daure dansa Ishaku, ya kwantar da shi akan bagadi. Zai kashe dansa kenan, sai Allah ya ce, ''Dakata! Kada ka yi wa yaron rauni! Yanzu na san kana tsorona, domin baka hana mani danka tilo ba."

OBS Image

A kusa da wurin Ibrahim ya ga rago a sarkafe cikin daji. Allah ya riga ya tanada ragon hadaya amaimakon Ishaku. Da farin ciki Ibrahim ya mika ragon hadaya.

OBS Image

Sa'annan Allah ya ce wa Ibrahim, "Saboda ka amince ka bani kome, harma danka tilo, Na yi alkawari in albarkace ka. Zuriyarka zata fi taurarin sama yawa. Domin ka yi mani biyayya, dukkan iyalan duniya za su zama da albarka ta wurin iyalinka.''

Labari a Littafi Mai Tsarki daga: Farawa 16-22