ha_obs/content/04.md

2.7 KiB

4. Alkawarin Allah da Ibrahim

OBS Image

Shekaru da dama bayan ruwan tufana, mutane suka sake yawaita a duniya, kuma yare daya su ke yi. Maimakon su cika duniya kamar yadda Allah ya umarta, sai suka taru dukka suka gina birni.

OBS Image

Su na cike da girman kai, ba su kula da abin da Allah ya fada ba. Harma suka fara gina hasumiya mai tsawo da zai kai sama. Allah ya ga idan suka ci gaba da aiki tare domin aikata mugunta, zasu iya aikata wassu zunubai ma fiye da haka.

OBS Image

Saboda haka Allah ya sauya harshen su zuwa harsuna daban daban sai ya warwatsar da mutanen a dukkan duniya. Birnin da suka fara ginawa aka ce da shi Babila, ma'ana, "rudani."

OBS Image

Bayan shekaru aru-aru, Allah ya yi magana da wani mutum da ake kira Abram. Allah ya ce masa, "Ka bar kasar ka da iyalin ka ka je wurin da zan nuna maka. Zan albarkace ka in kuma maishe ka al'umma mai girma. Zan kasaita sunan ka. Zan albarkaci wadanda suka albarkace ka in kuma la'ananta wadanda suka la'ananta ka. Dukkan iyalan duniya za su sami albarka saboda kai."

OBS Image

Sai Abram ya yi biyayya da Allah. Ya dauki matarsa, Saraya, tare da dukan barorinsa da kuma duk abinda ya mallaka, ya tafi kasar da Allah ya nuna masa, kasar Kan'ana.

OBS Image

Sa'anda Abram ya iso Kan'ana, Allah ya ce, "Ka dubi kewayanka. Zan baka, da kai da zuri'arka iyakar kasar da ka iya gani a matsayin mallakar ka." Sa'an nan Abram ya zauna a kasar.

OBS Image

Wata rana, Abram ya sadu da Malkizadek, firist din Allah Madaukaki. Malkizadek kuwa ya albarkaci Abram ya ce, "Bari Allah Madaukaki wanda ke da sammai da duniya ya albarkaci Abram." Sa'an nan Abram ya ba wa Malkizadek daya bisa goma cikin dukkan mallakar sa.

OBS Image

Shekaru da yawa suka wuce, amma Abram da Saraya har yanzu basu sami 'da ba. Allah ya yi magana da Abram ya sake yin alkawari cewa zai sami 'da da kuma zuriya mai yawa kamar taurarin sama. Abram ya gaskanta alkawarin Allah. Allah kuwa yace, Abram mai adalci ne domin ya gaskanta da alkawarin Allah.

OBS Image

Sa'an nan Allah ya yi alkawari da Abram. Alkawari kuwa yarjejeniya ce tsakanin mutum biyu. Allah ya ce, ''Zan baka 'da daga jikin ka. Na bada kasar Kan'ana ga zuriyar ka.'' Amma har yanzu Abram ba shi da 'da.

Labari a Littafi Mai Tsarki: Daga Farawa 11-15